Sunday 18 February 2024

Ina ruwa na!

 

Rana ta take gari kuma yayi tsit, sai karar iskar bazara na tayar da kura. Na Audu na zaune a gefen hanya yana sake-sake a ransa dangane da kuncin rayuwa. Cikin lokaci kankani sai gashi ya tsunduma kogin tunani yana tarawa yana debewa. A wannan yanayi ya fada tunanin halin da yake ciki da kuma sanadin halin da alumma ta tsinci kanta. Ganin mai ruwa na tafiya sai ya tuna masa da zancen bayaushe na ina ruwa na idan yana ganin abu bai shafe shi. Kamar maganar wai idan jifa ya wuce ka to ya fada kan kowa! Me za ka rasa idan ka hana jifan daga faruwa ko kuma idan ya wuce to ka taimaka  kar ya fada kan kowa don ka da ya yi illa? Me yasa baza ace idan jifa ya wuce ka, ka taimaka don kar ya cutar da kowa ba? Na Audu na ganin haka ya dace to kana zargin wannan karin maganar akan halin da alumna ke ciki kenan? Tambayar da Hadi yayiwa Na Audu kenan. Na Audu ya gyada kai ya kada baki yace, a'a. Amma ina ganin idan mutum ya tarbiyantu da kalamai na taimako zai yi amfani wajen yadda zai bullowa alamura. Halin ko in kula da ya kawo mu cikin damuwa nake taajibi. Yanzu kaga a garin mu sai ka bada kudi kafin kayi bacci da sauran alamura na rayuwa! Kamar yaya, bari na Baka labari ko na fede biri har wutsiya. 

No comments:

Post a Comment